Top Local Places

Labarin Masoya

jatakatransformerline, Yakasai, Nigeria
Library

Description

ad

WANNAN SHAFI ZAIRIQA BAYAR DA SHAWARWARI GA MASOYA DAKUMA LABARAI DA SUKA SHAFI MASOYA

RECENT FACEBOOK POSTS

facebook.com

Nigeria Zaiyi matukar wahala anan kusa Nigeria ta iya gyaruwa, duba da yadda kasar kullum take kara lalacewa, Mutanen da suke da zuciyar gyarawa anabinsu ana kashewa kuma an dabi'antar da Sauran talakawan akan son zuciya da handama da babakekere, Abinda yake bani tsoro shine idan kakalli kunshin Gwamnati daga Sama har kasa zakaga masu sonzuciya barayi suke da rinjaye, wadanda kullum tunaninsu aljihunsu ba kasarsuba, Idan kajeka Makarantar Primary yanzu haka kasamu yara 'yan aji uku zuwa biyar ka tambaye su daya bayan daya, Kowanne inyagama karatu meyake son yazama zakaji irin amsoshin dazasu baka na tashin hankali, Domin karamin yaro dan primary anda bi antar dashi akan inyagama karatu yasamu aiki shine yasamu kudi yagina gida ya sai mota. Zaiyi wahala acikin yara dari ka iya samu biyar masu tunanin insungama karatu zasu taimaki kasarsu zasuyiwa kasarsu aiki Da wannan nake ganin zaiyi matukar wahala a irin nawa dan karamin tunanin Nigeria ta iya gyaruwa domin manyan goben tunaninsu daya da manyan kuraye da birgaye, beraye dake mulki yanzu akasar. Dan haka wannan abu yana bani tsoro matuka anya Nigeria zata gyaru kuwa? Wannan itace tanbayar danake yiwa kaina ako da yaushe idan zata gyaru shin wasu mutanen za akawo daga wata kasar su gyara? Indai 'yan Nigeria ne to hatta 'yan primary kusan tunaninsu daya da wadanda suka lalata kasar! Ta yaya kuke hangen ko tunanin Nigeria zata gyaru?

facebook.com

MANSA MUSA - Mutumin da yafi kowa arziki a tarihin Duniya. A 'yan kwanakin nan naga wani labari da wata kafar sadarwa ta Internet ta wallafa, na Mansa Musa a matsayin mutumin da yafi kowa arzihi a tarihin duniya, wannan labarin naga ya haifar da cece kuce da mahawara. Abnda na lura dashi shine a kasarin mutanen da suka musanta wannan labarin sun fito ne daga kudancin kasar nan, meyuwa abinda yasa suke karyata wannan labarin saboda sunga Mansa Musa, a tunaninsu zai iya zama Bahaushe ko Fulani, su Kuma suna ganin Hausa Fulani basu dace da wannan matsayin ba. Ba za a taba raba Hausawa da Fulani ba, kamar yadda ba za a taba raba Fulani da kabilun Mali ba. Idan aka bi wata salsalar za mu iya fanimtar cewa Sarki Mansa Musa mutumin da yafi kowa arziki a tarinhin duniya yana da alaka da Hausa da Fulani. Waye Mansa Musa ? Littattafan Tarihin Musulunci dama wadanda Turawa suka rubuta sun kawo tarihin wannan mashahurin Sarki, da bunkasar Masarautarta. Sarki Mansa Musa (Musa Keita) ya hau kan ragamar mulki ne a shekarar 1312 bayan rasuwar Sarki Abu Bakr na biyu. Hawansa karagar mulki ke da wuya ya fada iyakar masarautarsa tun da gabar ruwan Gambia, har yankin kasar Sudan, yankin kasar Hausa dake Nigeria da kasar Nijar da Senegal, Burkina Faso, maki, Gambia, Mali, Chad da Mounretania su suka hadu suka bayar da Daular da Mansa Musa ke mulka. Babban birni ta shine Tumbukhtu wanda yake a kasar Mali a yanzu. Sarki Mansa Musa ya shmfida mulki na kasaita, ya Kuma fada birnin Tumbuktum ta yadda yayi gogayya da manyan birenen duniyana wancan zamanin. A shekarar 1324 Mansa Musa ya shirya tafiya kasar mai tsarki domin sauke Farali, tafiyar da ta barwa dubiya tarihi na ban mamaki. Lokacin a tawagar Sarki Mansa Musa ta motsa daga birnin Tumbuktu zuwa garin Makka, ya tafi da sojoji sama da dubu ashiri, bayin da za suyi hidima sun haura dari biyar, ya debi dukiyar dukiya da zummar yin hadaya a kasa mai tsaki, dukiyar da ko sarakunan Daular Larabawa basu taba mallakar irinta ba. Kamr yadda malaman tarihi suka Ambato, sunce da rakuma dubu ashirin da dawakai dubu shida, da manya manyan mazuban Zinare a azurfa, da tufafi masu alfarma da sauran nau'ikan dukiya domin bayar dasu kyauta ga mutanen Makka da Madina. A lokacin wannan tafiya tasa ya tafi da wata amaryarsa wacce yake matukar kauna, lokacin da ya ratsa Saharar arewacin afirka, bayan tafitar watanni, sai amaryarsa ta gaji da tafiya a cikin Sahara, inda saboda kaunar da yake mata ya umarci da a share Saharar a kirkiri dausayi (Lambu) domin ta huta. A tarihin duniya wannan shine lokaci na farko da aka taba samar da dausayi a cikin Sahara. nace na yanka sama da rakuma dubu uku akayi amfani da ruwan cikinsu akasa samar da wani Dausayi mai tarin ni'ima da shuke shuke masu ban sha;awa. A wannan Dausayi amaryarsa ta samu damar hutawa har na wasu watanni kafin daga bisani, tawagar ta sake motsawa. Labarin wannan tawaga ta ratsa ko ina a kasashen Yankin Magrib, sarakuna da da dama sun kadu sun Kuma firgita da karfi da Kuma tarin dukiyar da suka gani ta Sarki Mansa Musa. Lokacin da wnnan tawaga ta iso kasar Misira, ya kidima mutanen kasar basu taba ganin mutum mai karfin dukiya kamarsa..Yadda ya kusan mayar da Misirawa bayinsa saboda tarin dukiyar da ska gani. Zan ci gaba.

facebook.com

455414m 414!kum 84rk4nku d4 w4nn4n 10k4(h! !n4 f474n kunwun! 14f!y4 y4 4k4j! d4f474n 24mu k454n(h3 (!k!n k05h!n 14f!y4 n490d3 d494 n4ku pr!n(3 h4554n k4n0

facebook.com

Kisan Gilla Da Aka Yi A Ile Ife Da Matsaloli Masu Tasowa Daga Mahmud Isa Yola Mu muna nan ne a Arewa ba a jihar Osun ba. Amma labarin da yazo mana shine: wani dan Arewa matashi ya mari matar wani Taana (kuyi hakuri na kira shi da sunan Taana saboda shine ƙurewa a kasanci) a bakin shagon ta. Daga nan ita kuma ta kira mijin ta Tana ta sanar dashi abunda ke faruwa shi kuma ya gayyato ‘yan uwan shi, suka kashe iya abunda zasu iya kashewa cikin mutane sannan kuma suka wawuri dukiyan jama’a iya son ran su. A cikin wannan labari akwai abubuwa guda biyu ma banbanta. Idan da labarin ya kasance cewa wani bahaushe ya mari matar wani bayarbe ne, sai bayarben ya zo don ramuwa, kuma ya rama mata, ko kuma ya gayyato mutanen shi suka rama wa matar kan Bahaushen da yayi marin, to wannan ba sabon abu bane kuma a matsayin shi na namji yana da hakki yabi kadun matar shi. Amma abun ya kai ga kisan mutane wadanda basu ji ba basu gani ba har sama da mutum ashirin, wannan wani babban abu ne na daban. Ina nufin zarcewa da suka yi har suka kashe mutane sama da ashirin, ba yana nuna wa cewa ramuwar gayya suke yi ba. Abun da wannan yake nuna wa shine dama suna cike da wadannan Hausawa dake zaune tare da su. Sun jima suna neman sanadi amma sai yanzu suka samu, wannan yasa rikicin da ya shiga tsakanin Bahaushen nan da bayarbiya nake ganin shi abu na daban. Haka kuma kisan gilla da aka yi wa Hausawa mazauna garin Sabo, cikin Ile Ife shima nake ganin shi a matsayin abu na daban. Shi rikicin dake tsakanin matashin nan da bayarbiya rikici ne da ko yaushe ana iya samun shi tsakanin mutane biyu ko fiye, wannan yasa zakaga hatta harshe ma da hakori sukan yi sabani. Kuma ita matar idan har ya mare ta, tana da dama cikakke da zata nemi mijin ta don ita ba namji bace da zata fiskance shi. Amma kisan gillan nan, wannan wani mummunan makarkashiya ce da dama an dade ana shirya shi, an jima ana tsumayin ranan da za’a aikata hakan akan wannan mutane, yanzu kawai an samu sanadi ne abun ya bayyana. Sun far wa Hausawan nan ne da niyyan kassara su na har abada, sun kona musu shaguna. sun kwashe musu dimbin dukiyoyin su, sun musu kisan wulakanci tamkar dabbobi, wasu sun sassare su, wasu sun harbe su, wasu sun kona su da ran su! Yarbawa mazauna garin Ile Ife sun tabbatar mana da cewa duk abunda dabba zai aikata, to mutum zai iya aikata abunda ya fi shi. Ba rayukan Hausawan nan ne kadai suka hara ba, sun hari dukiyoyin su. Da dama na karanta labaru cewa sun rasa miliyoyi kudi, wannan wadanda suka tsira da rayukan su muke magana. Alamu sun nuna cewa wadanda suka aikata wannan aika aika sun aikata hakan ne a bisa dalili daya. Wannan dalili kuwa ba zai wuce kyashi da suke dashi akan habakar kasuwancin bakin su Hausawa ba. Garin na Ile Ife kuma gari ne da yake da Hausawa fiye da kowani yanki a jihar Osun. Hausawa sun dade a wannan wuri, wasu ma na hasashen cewa garin Sabo gari ne da asali yake mallakan Hausawa. Babu shakka gwamnati ta dauki matakai da suka dace kawo yanzu, to amma wannan matsala ba ta gwamnati kadai bace, matsala ce da nake gani Sarakunan gargajiyan wannan yanki ya kamata su warware. Kaman yanda na sha fada a rubutu na cewa, mutane sun fi kusa da wadannan shuwagabanni fiye da gwamnati, kuma su din sune shuwagabannin abun da ake fada akai, wato kabilu. Wannan yasa nake gani sune ya kamata su fara kiran al’umman su su gargade su akan illan abunda suke aikatawa. Akwai ‘yan uwan su a Arewa, yau da gobe ba abun da ya bari. Hakan da suke yi suna jefa rayuwar ‘yan uwan nasu ne cikin hatsari. Haka kuma fa idan sun manta ya kamata su tuna, Hausawan nan da suka yi wa kisan wulakanci fa ‘yan kasuwa ne da suke sayar da kayan masarufi da ba’a noma su a kudu. Idan har suka kashe su, to ina makomar masu bukatan kayakin su? Naga wani hoton gawar wani an kashe shi a wurin sana’an shi, gawan shi na kwance akan Albasa da yake sayarwa. Abunda na fara tunawa da naga wannan shine tunda sun kashe shi, wa zai kawo musu Albasa kuma? Yanzu haka da dama Hausawa mazauna garin, wadanda sun riga sun yi jijiya a garin suna dawowa Arewa. Wannan babban koma baya zai jawo wa ‘yan garin saboda zasu dau shekaru masu dimbin yawa suna ji ajikin su ta fannin kasuwanci. Kisan gilla wa wata kabila ko wace iri ce ba karamin illa bane ga cigaban kasa. Yin hakan da farko zai kara sanya gaba ne cikin zukatan wadanda abun ya shafa, sannan kuma zai kara janyo wata baraka a kasa. Kuma rikicin idan an fara shi zai rika tafiya ne ba iyaka. Wanda aka ci gaplaba akan ta zata koma shirya wa don ramuwa. Al’umman kasar Nijeriya ya kamata su gane cewa, zaman lafiya shine ginshikin cigaban kasa, idan har babu zaman lafiya to kasa babu yanda zata cigaba. Idan kuma kasa bata cigaba ba, to al’umman cikin kasar suna cikin tashin hankali a koda yaushe. Za’a iya samun marubuci a: 08106792663 (Text)

facebook.com

*LABARI MAI RATSA ZUCIYA* Wata rana a makarantar manya malamin koyar da sanin halayyar dan Adam (Psychology), ya shiga aji yace "yau zamu yi wani wasa", "me ? wasa". Malam yace a cikinku wa zai fito gaban allo a fara da Shi ? Sai wata daliba Salma ta fito. Sai mlm yace ta dauki alli (chalk) ta rubuta sunan mutane 30 masu muhimmanci a rayuwarta. Salma ta rubuta dangi, kawaye, abokan karatu da makwaftanta. Sai mlm yace ta goge 3 wadanda basu da muhimmanci sosai a wajenta. Salma ta goge suna 3 na abokan karatunta. Sai mlm yace ta kara goge 5 marasa muhimmanci, Salma ta goge makwaftanta. Malam yayi ta umartarta tana gogewa har sai da ya rage sunaye 4 kadai sune :- Babarta, Babanta, Mijinta da Danta 1 data haifa. Gaba dayan dalibai sai suka nutsu sun gane cewa wannan ba wasa bane kamar yanda Malam ya fada da farko, yazo musu ne da wani darasi mai muhimmanci. To ! Sai mlm ya kalli Salma yace ta kara goge 2 daga sunayen nan da suka rage, wannan zabin fa yana da wuya, Salma tayi jimmm ! Hannunta yana rawa ba'a son ranta ba idonta ya cika da kwalla ta goge sunan Babarta da Babanta. Sai mlm yace ta kara goge 1. Sai Salma tasaka kuka ta goge sunan Danta 1 tilo. Sai mlm yace ta koma wajenta ta zauna. Bayan wani Dan lokaci sai mlm yayi tambaya, yace :- " me yasa ta bar mijinta" ? Iyayefa sune suka kawo ki duniya suka raine ki har kika girma. Danki kuma ke kika yi cikinsa kika sha wahalar laulayin cikin kika haife shi, kika raine Shi, kuma da iyaye da Da bazaki iya sake wadansu ba, amma miji ko yaushe zaki iya chanja wani. Aji akayi shiru ana jiran amsar Salma. Salma cikin nutsuwa da sanyin murya tace :- "Wata rana iyayena ina tare dasu suka dauke ni suka kaini gidan miji, idan na kawo musu ziyara sai su tambayeni, "lafiya" ? Idan yayi min laifi na taho gida sai su kira Shi suyi ta bashi hakuri, suce na tashi na koma gidansa". Dana kuma wata rana zai barni idan ya girma ya mai da hankali kan sana'arsa da hidimar iyalinsa. Mutum 1 wanda zai kare rayuwarsa tare da ni shine MIJINA, kuma...... Kafin ta kara magana sai dalibai suka dauki tafi gaba daya saboda ta fadin gaskiyar yanda rayuwa take. Sai mlm yace :- "Gaskiya ne, Allah ya sanya aure a tsakanin miji da mata ya zama dangantaka ta tsowon rayuwarsu. Ko yaushe ka girmama abokin rayuwarka (miji ko mata). Allah ya sanya miji da mata su zama Abu 1. Kamar yanda yazo a al- our'ani mai tsarki, Allah yana cewa :- " yana daga cikin ayoyinsa ya halitta muku matayenku daga jikinku, don ku rayu dasu, ya sanya a tsakaninku tausayi da jin kai, hakika a cikin wannan akwai aya ga ma'abota tunani". Don haka ku ( ma'aurata) ku zaku saka wannan dangantaka ta zama sama da kowace dangantaka a duniyar nan. Kafin mutum yayi aure Allah da manzansa sune a farko sannan dangi, bayan kayi aure Allah da manzansa suna farko miji/ mata sune na 2 Saman dangi. Ma'aurata ya zama wajibi ku baiwa aurenku abinci ya girma yayi karfi, abincin kuwa shine:-Bin dokokin Allah, Gaskiya, rikon amana, Hakuri, Zaman lafiya Soyayya da Nishadi. FATAN ALKHAIRI GA DUK MASU AURE.

facebook.com

Wannan shafi kwana biyu munrabu dayin post wannan yafarune sakamakon Ayyuka dasusha kan Admin wannan yasa muke Neman Admin Maza Biyu Mata duk wanda yake da bukata saiya Tura sako ga Admin na wannn shafi

facebook.com

facebook.com

Via…Salisu Lawal Dankaka (Abu_Abdallah) 02/05/1438 = 30/01/2017 Da Nassin Qur'ani Allah Tabaraka wata ala yatabbatar da Sahabban Manzon Allaj (S. a. w. )sune Masu imani na Gaske kayi nazarin wannan aya yakai dan uwa zaka fahimci inda nadosa. "WADANDA SUKAI IMANI SUKAI HIJRAH SUKAI JIHADI DOMIN ALLAH, SUKAI TAIMAKEKENIYA SUKA KARFAFESHI WADANNAN SUNE MUMINAINA GASKE,ZA AI MUSU GAFARA DAKUMA ARZIKI MAIGIRMA" Da wannan aya tacikin suratul Anfal Allah yatabbatar da imanin Sahabban Manzon Allah (S. a. w. ) domin sune sukai Jihadi sukai hijrah domin Allah duk wani Mai imani imaninsa ba tabbas bane nasu shine tabbas, Ko wanene komai girmansa komai matsayinsa Ba shehu ba ko wanene imaninsa babu tabbas domin baya cikin wadanda Allah yatabbatar da imanin na gaske ne. Malamina baiciki haka Malaminka shima baiciki Shehu na baiciki hakama Shehunka baiciki, sudindai Sahabbai wadanda sukai zamani da Manzon Allah (s. a. w. ) Sukai abokantaka dashi sukaci abinci tare dashi suka Aura raga wurinsa ya aura daga wurinsa yafita tare dasu suka fita tare dashi, To wadannan sune Masu Imani na gaske wanda basuba imanin sa ba nagas ke bane. Dan haka Lallai yakamata musani duk inda kaji Allah ya ambaci masu imani acikin Al'qur'ani To Ya ayyuhal ladhina amanu iri biyu ce. Tafarko itace kebantacciya kai tsaye da Sahabbai ake irinsu wannan ayar da makamancinta. Sauran kuma itace fadinta yake isowa har tashin kiyama Lallai dukkan Mumini na kwarai bashida abinso da girmamawa kamar Wadannan Muminai na gaske Ba daidai bane kafifita wani shehi ko waliyyi sama da wadannan domin su wadannan sune Masu Imani na Gaske Sauran Waliyyai da Shehunnai Imaninsu ba na gaske bane na tsammanine domin Allah bai tabbatar ba suko Allah yatabbatar da nasu imanin na Gaske ne. Allah kakara musu yarda damu baki daya kaganar damu gaskiya kabamu ikon binta kaganar damu karya kabamu ikon guje mata Naku :Salees Lawal Dankaka (Abu_Abdallah)

facebook.com

(HAQURI) kashi na (2) Tareda…:Salisu Lawal Dankaka (Abu_Abdallah) Khushu'i … shine gurmama Allah da kuma risina masa da kaskantar da kai a gabansa, Huzaifa yana cewa "AHIR DINKU DA KHUSHU'IN MUNAFURCI" Sai aka tambayeshi menene khushu'in munfaurci? Sai yace "SHINE KAGA JIKI YAYI KHUSHU'I AMMA XUCIYA BATAYI BA" yakuma ce "FARKON ABINDA ZAKU FARA RASAWA A ADDININKU SHINE KHUSHU'I" Kuma wata ibada da aka shardanta khushu'i acikinta, to girman ladanta ya danganta da yawan khushu'in mutum acikin ta, kamar Sallah saboda Manzon Allah (S. A. W) yace "DANGANE DA MASALLATA WANI BAZAI SAMU KOMAI BA CIKIN LADAN SALLARSA SAI RABINTA KO RUBU'INTA KO KHUMUSINTA HAR ZUWA USHIRINTA WATA KILAMA BAZAI SAMU LADAN KOMAI BA, SABODA RASHIN CIKAR KHUSHU'I" FATA…Shine duba izuwa fadin rahamar Allah, kishiyarsa kuma shine debe tsammani. Yin aiki bisa fata shiyafi da yinsa akan tsoro domin yi akan fata yake sanya mutum ya kyautata wa Allah zato, Allah yana cewa "NI INA NAN AYADDA BAWANA YAKE ZATONA" Shima yamasj kashi biyu: mafi daukaka shine kamar mutun yayi aikin da'a yana fatan samun lada Nana Aisha (R. T.A) tana cewa "YA MA AIKIN ALLAH FADIN Allah "KUMA SUNE SUKE BAYAR DA ABINDA AKA BASU ALHALI XUCIYARSU ARAZANEN" Shin sune masu sata da xina da shan giya shiyasa suke tsoron Allah? Sai Manzon Allah (S. A. W)yace "BA HAKA BANE YA 'YAR GIDAN ASSADIQ, WADANNAN SUNE SUKE SALLAH SUKE AZUMI KUMA SUKE BAYAR DA SADAKA, TARE DA HAKA SUNA TSORON KAR AKI KARBAR SADAKAR TASU" Wadannan sune masu rige_rige wajen ayyukan Alheri " Daraja ta kasa… shine mai laifi idan yatuba yayi fatan samun gafarar ubangiji, amma mai laifi da yake dawwama akan laifinsa, kuma baya tuba kuma yazamo yana fatan samun rahamar Allah, wannan buri ne kawai ba fata ba. Kuma irin wannan shine xargi amma na farko shi ana sonsa, Domin mumini shine wandda ya hada tsakanin ihsani kyautata aiki kamar yana ganin Allah da tsoro shi kuwa munafuki shine wanda ya hada tsakanin munana aiki da kuma nitsuwar xuci ruduwa kamar ba laifi yayi ba. TSORO…shine damuwar datake riskar xuciya saboda sa ran abkuwar wani abu da ba aso, idan an tabbatar da faruwar abin kin, to ya zama "ALKASHYA" kishiyar wannan kuma aminci. Shi tsoro ba kishiyar fata bane yana faruwanedaga fargaba shikuma fata yaba faruwa ne daga kwadayi. Kuma dole ahada tsakanin soyayya da tsoro da fata. Ibn kayyim yana cewa "ZUCIYA KAMAR TSUNSTU TAKE A LOKACIN DA TAKE TAFIYA XUWA GA ALLAH SOYAYYA ITACE KAN WANNAN TSUNTSU, TSORO DA FATA KUMA SUNE FUKA_FUKAI" Don haka idan tsoro ya kame xuciya sai ya kone guraban sha'awa acikinta ya kuma kore son duniya. Tsoro na wajibi… shine wanda yake sanya mutum ya aikata abubuwan dasuka wajjaba agareshi, ya kuma bar abubuwan da suka haramta. Shi kuma Tsoro na Mustahabbi… shine wanda yake sanya mutum ya aikata ayyukan da suke mustahabbai, ya kuma bar makaruhi Amma ya karkasu (1)Tsoron sirri kuma na ibada, wannan dolene yazamo ga Allah kawai idan akayiwa wanin Allah to anyi babbar shirka, kamar yadda mushrikai suke jin tsoron gumakansu don karsu cutar da su kokuma su haifar musu da wani abinki. (2)Wanda ya haramta shine barin wajibi ko aikata haram don tsoron mutane.(3)Wanda ya halatta kamar tsoro na dabi'a kamar mutum yaji tsoron kura ko wani abu makamancinta. Mu hadu akashi na uku Naku Salees Lawal Dankaka (Abu_Abdallah) 30/04/1438 =29/01/2017

facebook.com

(~~<>HAQURI………) # Salees Lawal Dankaka# Haquri shine barin kai kukan radadin bala'i zuwa ga wanin Allah, da kuma juyar da kai kukan zuwa ga Allah shi kadai. Allah yana cewa "ANA CIKAWA MASU HAQURI LADANSU BA TARE DA QIDIDDIGA BA" Manzon Allah (s. a. w) yace " DUK WANDA YAYI QOQARIN YIN HAQURI, ALLAH ZAI TAIMAKA MASA WAJEN YIN HAQURI, KUMA BABU WATA KYAUTA DA AKA BAIWA DAYANKU DATA KAI KYAUTAR HAQURI"bukhari da muslim ne suka ruwaitoshi. Sayyadina Umar (r.a) yana cewa"BABU WANI BALA'I DA YA TABA SAMUNA FACE SAI ALLAH YASANYA MIN NI'IMOMI HUDU A CIKI: TUNDA BAIZAMO ACIIN ADDININA BA KUMA BAI ZAMO FIYE DA YADDA YAZO GIRMA BA, KUMA BA A HARAMTA MIN YARDA DA SHI BA, KUMA INA NEMAN LADA AKANSA. " HAQURI HAWA_HAWANE… Mafi kankanta shine mutun ya bar kai kukansa tare da kyamar bala'i, Matsa kaici: shine barin kai kuka tare da yarda da bala'in Mafi girman daraja: shine godiya ga Allah akan bala'i, duk wanda yayi bakar addu'a ga wanda ya zalunceshi to haqiqa ya kwatarwa kansa haqqinsa, kuma bai yi haquri ba. HAQURI YA KASU GIDA BIYU… (1) Haquri na jiki ba akansa muke maganaba anan (2)Haquri na zuciya wanda ake akan abubuwan da rai yakeso, zuciya take sha'awa Duk wani abu da mutum yake gamuwa da shi a duniya, bazai fita daga dayan biyu ba. (A)Ko dai abin da ya dace da son xuciya wannnan yana bukatar haquri domin isar da haqqin Allah acikinsa na godiya da kuma rashin juyar da wani abu daga cikin zuwa sabon Allah. (B)Abin da yabawa son xuciya shima kuma wannan ya kasu kaso biyu (1)Haquri akan yiwa Allah da'a dan haka ya wajaba, ayi hakuri wajen aikata wajibai kuma ana so ayi haquri wajen aikata nafiloli (2)Haquri akan sabawa Allah ya wajaba ayi haquri wajen barin haram, kuma anaso abar abinda yake maka ruhi (3)Haquri akan Qaddara wajibine mutum ya kame bakinsa ga barin kai kuka, kuma ya kame Xuciyar sa ga barin suka da kuma fushi da Qaddara, ya kuma kame gabbansa ga barin yin abin da xai fusatar da Allah kamar koke_koke lokacin mutuwa, da kuma marin kunci da yaga tufafi da sauransu. Abinda kuma aka so mutum yayi acikin wannan kaso shine xuciya ta yarda da abin da Allah ya Qaddarah. SHIN WAYAFI FALALA TSAKANIN MAWADACI MAI GODIYA DA KUMA TALAKA MAI HAQURI?… Idan dai mawadaci yatafiyar da dukiyarsa wajen yiwa Allah da'a na wajibi da mustahabbi ko kuma ya adana ta domin hakan to yafi talaka, amma kuwa idan ya xamanto ya kashe mafi yawan dukiyarsa ne akan abinda ya halatta, to talaka yafishi. Manzon Allah (s. a. w) yana cewa "MATSAYIN MAI CIYARWA KUMA MAI GODIYA KAMAR MATSAYIN MAI AXUMI NE MAI HAQURI" ahmed ya ruwaitoshi. YARDA… shine mutum yasamu wadatar xuci ta yadda xai gamsu ya wadatu da abu duk karancinsa wannan ya kan faru ne bayan aiki ya abku, kuma ya yarda da abinda Allah ya Qaddara ma mutum na daya daga cikin manya_manyan darajojin makusantan Allah, shikuma sakamko ne na Soyayyah da ta wakkali kuma don mutum ya roqi Allah yakawar masa da wani abin ki baya kore masa yarda dashi.……………… Muhadu akashi n biyu Naku Salisu Lawal Dankaka (Abu_Abdallah) 28/04/1438 =27/01/2017

facebook.com

^^^^^^^^^BAQIN DUHU 2....^^^^^^^^^^ >>>>>>>>>Sadik kansa asunkuye yai ajjiyar zuciya ahankali yakakalo wani miyau maidaci ya hadiyeshi dakyar yace " Br. adukkan ma aikatan dake karkashina kosamana akamfanin nan bana zargin kowa saidai wani abu dayataba faruwa dakuma wani kallon raini danaga Alh. Tanimu wan marigayi yanamin musamman lokacin da aka karamin matsayi nazama General bayan bukinmu da Sadiya" Br.yace hakane bisa dukkan alamu binvikenan zai karkata zuwa kan Alh. Tanimu wala alla nasamo mafita.......lo kaci yayi inji ganduroba nan yatasa keyar Sadik yamaidashi cikin gidan kaso. Br. Salisu yatashi yazunguri motarsa yanufi gidan Alh.Musa marigayi sirikin Sadik wanda ake zargi da kasheshi. yai sallama yashiga Hajiya Talatu matar marigayi ta amsa tare dacewa shigomana Br. ahankali ya sadda kai yana haiaheta ta amsa. tasanshi don tasan shine lauya maikare wanda ake kara harga Allah tanaji aranta Sadik bazai iya kashe mutunba balle sirikinsa Alh. wanda yataimakeshi arayuwa yaimasa riga da wando kai abinda kamar wuya. amma tayaya zata karyata abinda yake azahiri na kama Sadik da gawar Alh. acikin But dinsa!.......gyaran muruar Br. yadawo da ita hayyacinta yadubeta yace " Hajiya kamar dai yadda kikasani sunana Br. Salisu Inuwa nine lauyan dake kare wanda ake tuhuma da kashe Maigidanki Alh. Musa" Hajiya Talatu tanisa tace nasani Br. yanzu meyakawoka? Br. yace "bincikene yakawoni dakuma amsar wasu yan tambayoyi danake fatan zaki amsamin" Hajiya Talatu tace karka damu ashirye nake nabaka amsoshin dukkan Tambayoyin dazakamin.... Br. yanisa yace nagode Hajiya. akaro nabiyu yasake kallonta yace "Hajiya aranar da Alh. yarasu kozaki iya tuna dawacce mota yafita kuma wadanne abubuwa yafidasu ahannunsa sannnn ina yace miki zashi? Hajiya Talatu....to Alh. yafita da mota kirar Camry ruwan makuba lambar Dala. kuma yafita da ayar hannu guda biyu Nokia da Samsung sannan yafita da wasu takardu acikin wani file danake tsammanin takardun kamfanin sane da tuma turin gwangwani zaibawa Sadik kamar yadda yasanar dani awa daya kafin yaiwanka yafita. shiru ta ratsa wurin tsawon mintina bawanda yace komai can Br. yanisa yace lallai wannan lamari akwai faure kai.......daidainan yaji muryar Alh. Tanimu yanafadin waya gaiyatoka kazonan gidan? tashi kafita karna sake ganinka anan gidan.....ke Hajiya Talatu tayaya zaki rika barin Lauyan wanda yake kare wanda muke zargi da kashe Alh.? yanuna masa hanya tashi kafita kuma karna sake ganinka anan giran........Hajiya takatseshi haba Alh. yakamata abashi hakkinsa na Lauya dan gudanar da bincikensa......au lallai Hajiya Talatu bakida hankali.....fuuu yashige cikin gida abinsa yana balbalin fada. <<<<komaifa yarikicewa Br. Salisu yarasa takamaimai hujjar kamawa gakuma kwanaki suna kara matsowa nakomawa kotu amma haryanzu babu wata kwakkwarar hujjar dazaigabatarwa kotu dan wanke wanda ake zargi..Tirkashi ya furta adaidai lokacin dayai parking motarsa adaidai kofar gidan Alh. Habu aboki ga marigayi Alh. Musa mainaira cikin sa'a sukai kacibus yana kokarin futowa daga gida. yamika masa hannu suka gaisa Br. yace Sunana Br. Salisu Inuwa nine lauya maikare wanda ake zargi fa kashe Abokinka Alh. Musa nazo wurinka dan kataimakamin da amsar wasu tambayoyi danake tafe dasu.... Alh. Habu yanisa yace inajinka :- Br. Salisu yakalli Alh. Habu yace aranar da kasami labarin rasuwar abokinka yakaji aranka?............. akwai rigima kada dai kugaji .........

facebook.com

ுுூBAQIN DUHU....1िििूुू "Ya mai shari'a ina roqon wannnn kotu mai Albarka data dubi hujjojin da muka gabatar agabanta na tabbatar fa mailefi ta yankemasa hukunci daidai da abinda ya aikata nagode ya mai shari'ah" Alkali:-ko lauyan wanda ake kara yanada hujjojin dazai karen wanda ake kara? Br.Salisu yamike jiki ba kwari yace " ya mai shari'a ina roqon wannan kotu mai Albarka data qara daga wannnn shari'a don gabatar mata da hujjojina wadanda zasu tabbatarwa da kotu Sadiq bashida laifi nagode ya mai shari'ah" Alkali:-bisa hujjoji da aka gabatar gaban wannan kotu basu isa sigamsar da kotuba adan haka kotu ya dage wannan shari'ah zuwa ranar 12-2-2012 kooootu...... @@@@yahada uban gumi kota ina zufa karyo masa takeyi ganin yarasa tudun dafawa danganin yaceto Sadiq daga wannan masifa da yake ciki yasani bashida laifi amma wavce hujja kwakkwara zaigabatar agaban kotu wacce zata wanke wanda ake kara? wannn itace tambayar daya kasa bawa kansa amsa Br. Salisu kenan ahanakali yaji saukar hannen matarsa Fanazarah agadon bayansa yai ajjiyar zuciya tace " haba yaya yanzu karfe nawa duba agogo fa? 12:30am yagada azuciyarsa sannun ahankali Fanazarah takwanta akan bayansa tanacewa Yaya katagewa kanka wannan zuzzurfan binciken haka kana kokari dukda kasan ba biyanka za"aiba amma kana iya kokarinka kayi hakuri tunda kakasa samo hujjojin dazaka wanke wanda kake karewa domin bisa dukkan alamu wadanda suka shirya wannan kisan gillar da wannan makircin ashirye suke suga bayan duk meneman tona musu asiri" ahankali Br. yai ajjiyar zuciya yace karki damu kedai kici gaba dayimun addu'a insha Allahu Allah yana taredani domin na tabbatar nike da gaskiya kuma zanyi nasara insha Allahu. ........kirrrrrr....kirrrrr.....kirrrr...... wayarsa dake gefe tadau kururuwar neman agaji Fanazarah ta dauka takaramasa akunne Muryar dayasaba jice tun lokacin dqwowarsa daga Malesia amatsayin Br. ya iske wannn shari'a maisarkakkiya ake kiransa ana razanashi akan wanda yake karewa cikin kakkausar murya aka furta " Br. kanada taurinkai saunawa zamugayama ka ajjiye wannnn Case din amma kaki dan tsabagen taurinkai irin naka. ok kazabi kaima karasa ranka kenanko? cikin tsawa Br. Salisu yace kai malam dakata kalamanka bazasu yaba tsorataniba akan abinda natabbatar inakan gaskiya inada tabbacin Allah zaitaimakene akanku kuma dasannu asirinku zaitonu........ ...dot...dot..dot... yaji wayar ta katse Fanazarah dake bayansa tace haba Yaya kahaukura da Cas dinnan koma tsira daga sharrin wadaddan miyagun.....ahan kali Br. Salisu yai ajjiyat zuciya tare da rungumota jikinsa yace kwantar da hnklinki kici gaba dayimun Addu'a insha Allahu zanyi nasara akansu....murmushi tayi tace; Yaya dadina dakai akwai tawakali ina goyin bayanka Allah yataimkeka yaimaka jagora maigidana nakaina muje mukwanta daya saura..... kwanaki suna shudewa amma Br. Salisu baisami wata kwakkwarar shaida dazai iya habatarwa da kotuba dan kare wanda yake kara. da sanyi safiyar ranar asabar Br. yashirya yanufi gidan kurkuku inda ake cigaba da tsare Sasiq wanda ake zargi da kashe sirikinsa uban matarsa Sadiya daidai karfe gate yai parking motarsa kirar Honda Henecy yashiga cikin gidan kurkukun inda yanemi izinin ganin wanda yake karewa wato Sadik. minti biyar Sadik yafito daure da ankwa hannu da kafa yai baki yarame yazauna kan dan dukurkushin benci shima Br. yazauna yadauko Laptot dinsa ya kunnah sannn yakalli Sadik yace "malam Sadik nayi iya kokarina wajen kareka amma abin yana neman faskara don nagagara samun kwakkwarar hujja wacce zan wankeka daga wannn zargi da akema. amma kozaka iya fadamin kafin Rasuwar Alh.Musa sirikinka acikin kanfaninsa daka rike mikamin General manager ko akwai wanda kuke takun saka dashi da harkake ganin zai iya yima wannan sharrin? yanzu akafara kubiyoni dan jinwannan sarkakken labari mairikitarwa da ilimantarwa........

facebook.com

Quiz

NEAR Labarin Masoya