Top Local Places

Muryar Matasan Nigeria

, Maitama, Nigeria
Media/news/publishing

Description

ad

Munayi muku barka da zuwa wannan shafi mai albarka na matasan Nigeria Kukasance tare damu. MoreAt www.hausagurus.com

Phone Number: 08064211468

CONTACT

RECENT FACEBOOK POSTS

facebook.com

Tech Vibez

Full Neco 2016 Subscription at WWW.EXAMPORTALZ.COM List of 2016 NECO subjects available English, Maths, Biology, physics, Chemistry, Literature, Economics, Commerce, Accounting, Agric, Goverment, Geography Office pratice, Marketing, Insurance, Data Processing, Further maths(not certain) I.C.T(Compulsory), Civic Education(Compulsory), Practicals: Agric, Physics, Chemistry, Biology. ====================== (i) ALL SUBJECTS practicals: N5,000 (text 09029063951 or 08102695893 before paying) (iii) 6 Subjects Practicals or no practical: N4,500 CARD (iv) 5 Subjects Practicals N3,000 MTN CARD (v)Payment for link all subjects practical: N5000 MTN CARD (vi)8/9 subject links subscription : N2500 MTN CARD (vii) All subjects scanned copy for center owners(text 09029063951, 08102695893) ====================== HOW TO SUBSCRIBE -PLAN PAID FOR (eg: 6 SUBJECTS PRACTICALS) -SUBJECTS -MTN CARD -PHONE NUMBER(MTN) -NAME -AMOUNT PAID send it to 09029063951, 08102695893 ====================== DO NOT SUBSCRIBE WITH AIRTEL/GLO LINE, MTN is PREFERABLE ANSWERS WILL NOT BE POSTED FREE OF CHARGE so don't deceive yourself . BENEFIT OF PAYMENT BEFORE EXAM: (i)You will be registered on our database where u can confirm ur subjects to make sure there is no mistake on ur subjects (iii)You will get special attention from us. For more info; Whatsapp; 08102695893 Facebook: www.facebook.com/exa mportalz Twitter: www.twitter.com/examp ortalz emails: samiulhaqqq@ gmail.com

facebook.com

Shirin Rai Dangin Goro yazo da sabon salon tarwatsa tarbiya A gaskia ba qaramin illa da matsala gami da tabarbarewar halayya da tarbiyya shirin karatun littafin da ake yi a wasu kafaffen yada labarai a jihar kano ke qara asasawa ba, shirin Rai Dangin Goro da Zaman Dunia da wasu qafafen yadda labarai ke dauke mintina kusan talatin suna sanyawa ta muryar wani gwani wajen sarrafa harshe a karanto tatsuniya da qarshen bai wuce Qurus Qus ba. Abin takaici a yayin da ake kukan tagarde sai ga karaya ta samu, a lokacin da malaman makaranta kan qi shiga ajujuwansu, dalibai qan qauracewa darussan su, likitoci kan jinkirta ganin Patients din su, matan aure kan qauracewa mazajen su, masu neman abinci kan sakaci da neman su, 'yan Adaidaita Sahu kan wasa da rayyukan fasinjan su, ma'aikata kan sabawa dokar aikin su, iyaye kan wancakalar da diyoyin su, da sauran abubuwa da dama da ake ajjiyewa walau ya dace a ajiye ko bai dace ba da zarar Qarfe 9:30 na safia ko 6:00 na yamma sun yi tare da rungomo akwatunan radiyo ko maqale abin Jin magana a radiyo da bada kulawa da nutsuwa ta musamman sai gashi a kara kunno wani bala'in. Gaskia irin abubuwan da suke faruwa da sakancin da ake fuskanta dan gane da masu sauraron waddan nan shirye_shirye tatsuniyoyin akaran kansu ma illah ne, abin mamaki sai wata sanarwa tana yawo wannan da yake amfani da salon muryarsa wajen karye_karye da laqwashe_lanqwashe zai zo Kano don ganawa da masoyyansa da masu qaunarsa da sauraronsa abin takaici har da wani sanya kudi sai kace wani gaggarumin mutumin da duniya ko jama'a zasuyi alfahari da zuwansa ne zai zo, kai ya ilahihl alamina wannan abu da mai yayi kama. Ba zuwansa nasa ko ganin nasa ba ne illah, qaryar da mataye da mazaje zasu sharadawa waddanda suka isa ko suka ajiye su shine abin duba, nayi imani akwai waddanda tunda suka ji sanarwar sunanan suna kintsa ire_iren qaryar da zasu gayawa mazajensu ko iyayensu da sun samu su fita gobe dan ganin sa. Matasa masu sana'a ko dalibai suma na nan na kintsa kala_kalar qaryarsu, gayu 'yan bana bakwai kuwa sunan suna fafutukar samo sandunan daukar hoto don abin nema ya samu, matar direba ta haiffi kwandasta. A Gaskia gwamnati da hukuma musamman wadda take la'akari da gudanar harkokin shari'a su maida hankali da kallan abin da idon basira, bawai hana zuwan mutanen wajen kallon sa ba ne mafita, a'a wannan zaiyi wuya don a komai baka rasa waddanda basu san mai yake musu ciwo, abin yi shine a kula sosai da irin abinda zai ringa gudana a wajen musamman na haduwar Maza da Mata ciki ko a waje ko a motoci masu rufe da baqin leda, sannan Ai la'akari sosai gurum irin hotuna da za'a ringa dauka a wajen, babbar shawara bai kamata a bar koda macce guda indai matar aure ce ta shiga wajen ba, su kansu 'yan matan a bada kulawa ta musammman wajen ganin dacewa ko rashin dacewar shigar yarinya tun daga yanayin suturarta, kammallarta da sauran abubuwa, in da son samu ne ma a hana Mata shiga tunda masoya aka ce ai yana da 'yan uwansa Maza Sai suje su kalle shi. Gyara Kayanka. Prince Ahmad Amoeva #Wazapp 08066038946 #Twitter #Prince_Amoeva Kana iya ziyartar wannan daddalin Dandalin Prince Amoeva Don jin labarurruka, fashin baqi da ra'ayoyi masu ilmantarwa da qayatarwa. Don Allah a taimaka a yi sharing ko Copying don ceto 'yan uwa daga wannan balahirar. Allah ya kyauta.

facebook.com

Biyan Kudin Jarrabawar Kammala Sakandire A Gwamnatin Gadunje ( An bar dukan jaki ana dukan teki). Mai karatu zai yi tambaya shin mai yasa na yiwa rubutun take da sunan sama, lallai kam abinda yafi taken sama ma ana iya baiwa rubutun suna dashi. Tun bayan rantsar da sabuwar gwamnatin jihar Kano qarqashin mataimakin jagoran kwankwasia ta qasa sanata mai ci a yanzu tsohon gwamna Kano Engr Dr Rabi'u Musa Kwankwaso sha'anin mulki da gwamnatin take ta tafiar wahainia da tsallen kwado, yau kaji talakawa na kuka da wannan,gobe waccan jibi waddancan, an sha surutai da qorafi akan dawo da biyan kudi makaranta, qin ci gaba da tura dalibai 'yan asalin Kano qasashe qetare dama wasu daga cikin jami'oin mu na gida don samun garabasar karatu kyauta da gwamnatin baya ta qirqiro, dakatar da ciyar da dalibai abinci da tufatar da su da sauransu, ana cikin jimamin wannan sai gwamnati ta fito da wani tsarinta na biyan haraji wanda har wasu da jagororin gwamnatin suka fadi kalaman marasa dadi da sauraro kan biyan harajin, har takai an sha'awantawa wanda bazai iya ba yin hijira daga kanon zuwa wani waje daban, hakan ya zama tamkar cin fuska da musgunawa talakawan da Mai Girma Shugaban Kwamittin Aviation Sanata Kwankwaso ya roqe su dan ganin sun dangwalawa gwamnatin Ganduje, suka amsa roqon jagoran duba da ayyukan da ya shinfida don sun yi imani shima Ganduje zai yi haka tunda wanda aka hau tare tare ake fatan sauka, amma ashe da sake an harba kibiya sama ta maqale. Duk da ana cikin wannan juyin juya hali, talakawa da masu kishin su ba yadda suka iya face amfani da waraqa da tawada wajen gayawa gwanati gaskia a lokacin da masu baki da kunu ke qoqarin kare gwamnati da qodurinta da qarfin sakacin rashin hujja ko madogara, duk da cewa suna yi ne kurum dan kare haqqin tukunyar su da aljifunan su ba dan son buqasa ko tausayawa talaka ba. A wattanin baya an samu wata 'Yar hatsaniya a wata makarantar kwana ta maza a jihar Kano, wanda har kwamiti aka nada akan wannan balahirar, duk da cewa sun yi aikinsu yadda ya dace, makarantar dai makaranta kudi ce wadda kashi mai yawa na daliban 'ya'yan masu hanu da shuni ne, canzawa 'ya'yansu makarantu ba matsalar su ba ne, amma kwatsam sai aka ji gwamnatin Kano qarqashin Gwamna Ganduje sun cire wasu maquddan kudade an ware don biyawa daliban makarantar kudin jarrabawa, jama'a da dama sunyi ta maida albarkacin bakunan su akan batun amma a banza don aikin gama ya riga ya gama, haka zalika a yayin bikin fita da shigar daliban wata jami'a dake Jigawa gwamnati ta qara ware wasu maqudan kudaden da sunan tallafi ko taimako, tab wannan shine inuwar giginya.................., ilimi akace don haka damuwar bata yawaita a fuskokin kanawa tunda ma'abota son ilimi da taimako ne. Ranar 18_01_16 dadadden sakamakon daliban jihar Kano na chanchantar samun damar daukan nauyin gwamnati wajen biyan karatun kammala Sakandire da ake kira da suna Qualifying ya fito, ko shakka babu abinda ake ta rade_radi da qusin_qusin sakamakon zai nuna haka ya kasance, a shekarun baya tun lokutan gwmanonin baya su Mallam Ibrahim Shekarau da Sanata Kwankwaso ana biyawa dalibai jarabawa biyu (WAEC da NECO) amma wannan gwamnatin tace ita guda daya zata iya, wannan shima bai yiwa iyayen yara dadi ba amma ba yadda suka iya don in Har za'a biya musu guda dayan ai ' Labuh'asah' inji larabawa. Sakamakon ya nuna sama da kashi 70 na daliban basu samu damar tsalake siradi ba ko na ce sun fadi, cunkuso tare da nuna baci da damuwar shugabannin makarantun sakandire a hukumar ilimi da Rumfa College ya isa tabbatar ma akwai matsala. Abin tambaya: ta yaya za'a ce a makarantar da dalibai 140 ko sama da haka zasu zana rabawa amma ace mutum 1 ko 10 ne kurum suka ci? mai ya jawo tsawaita lokaci da riqe sakamakon ba tare da an sake shi da wuri ba? banda dawainiyar biyan kudin makarantar da gwamnatin Ganduje ta dawowa da iyayen yara wanda a sakamakon haka yayi sanadiyar barin dalibai karatu da dama, yayi sanadiyar rasuwar iyayen yara kan takaicin korar diyoyinsu daga makarantu, uwa uba ma yayi sanadiyyar Rasuwar wani Dalibi ( kamar yadda yau a labaran gidan wani radio aka shaida) take son qara dora musu wani biyan kudin? Gwamnati tasan cewa kudin WAEC da NECO zasu kai Naira 25000 ko sama da haka? Anya akwai tsoron mahalici da son ci gaban ilimi a wuyan wannan gwmanatin? Ba'a nan gizo ke saqar ba, in har gwamnati zata iya biyan wasu maqudan kudade ga wasu daliban makaranta da daukar wasu kudi ta bayar ga wata jami'a mai zai sanya a bar 'ya'yan talakawa da iyayen su a cikin wannan qangi? Anya kuwa gwamnatin nan ta Talakawa ce ko ta masu Hannu da Shuni? Su Daliban waccan makaranta Jarabawar qualifying din suka zana? In sun zana kuma dukan su ne suka ci? Ya kamata gwamnatin Ganduje ta fito ta amsa mana wannan tambaoyin ko iyayen yara sun danji sanyi a zuciyoyin su. Akwai fa 2019, Mallam Ganduje kar fa a manta! #StudenRigh #PayQualifying #NoMoreVias Prince Ahmad Amoeva 08066038946 #Twitter: prince_amoeva Yi like din Dandalin Prince Amoeva Don jin yadda take kanawa

facebook.com

Yar Mummy (Ummin Mama) Sillar Farko Taken qasar najeriyya naji wanda na tabbata wayana ne ke ruri, na sanya hanu na fiddo ta daga aljifuh, ba tare da na kalli wayar ba na dosana a kunne na na dama tare da fadin 'Sallamu Alaikum, Hello, da mamaki sai naji an sheqe da daria tare da fadin Hello tare da fatan kana lafia, kafin na budi bakina na qara magana wannan muryar ta qara ce min Kaima aminci Allah ya tabbata a gareka in ban batan sunaye ba ina magana da Prince Muhd na facebook, Prince Amoeva a Intagram, Prince Amoeva a Twitter haka zalika Prince Ahmad Amoeva a In da kuma Four Square, koda yake ka daina amfani ko yin charting din 2go amma shima in ban bata ba kana amfani da Amoeva. Kai na ya daure kafin nace komi muryar tace in banyi shishigi ba sunanka Ahmad N Muhd, but ur bearing Prince Ahmad Amoeva a cikin mutane da kuma decoment dinka wasu ko? Haka zalika kana Kano a anguwar.....................(abin mamaki abinda muryar nan ta fada dai-dai yake, lambar gidan mu, layin mu duk haka ne ba inda muryar nan tayi kuskure koda na daqiqa ne), muryar taci gaba da cewa nasan abu biyu ne yanzu haka yake faruwa ko yake wanzuwa a tattare da kai! Duk da na zauna sai zuba nake yi ma kamar danyar kanya, Don Allah kayi haquri na tabbata kana nan kana kule_kulen sakar min tambayoyi akan mai na kira ka? Wanene ni? Menene silar kiranka? Ya akai nasan wani abu daga mu'amalar ka, da dai Sauran tambayoyi dake ciki cikin zuciyarka! Kamar yadda nace abu biyu ke wanzuwa yanzu a fuskarka shine Farin ciki da alamamin tambaya ko ba haka ba? A karo na farko na bada amsa da Eh, amma don Allah........shiiiiiiiii akace dani ya isa, kai dai ka saurare ni amma Bana son magiya, na qara cewa toh amma ur credit yana qarewa, kusan minti 8 kenan, Hmmm muryar ta qara bushewa da daria sannan aka ce Amoeva kenan, wannan ba abinda ya shafe ka bane, ina iya awa 8 ina waya don Bana kiran mutum sai nasan ina da enough credit, ina fatan kana saurarana a nutse. Kamar yadda nace kar ka damu insha Allah da sannu zan fadama Who I'm I and also from where I'm calling you, so just be patient my friend. Nace Ok but na qagu naji, pls I beg ur Pardon tell mi know, lokacin Sallah Azhar na qara towa, so ina so naje..............Amoeva kenan Kaje ka kira sallah ko muryar ta qarasa abinda nake shirin fada. Mamaki ya qara mamayeni don kuwa na kadu da naji muryar tasan abinda nake shirin zuwa nayi, Amoevaa Amoevaa Prince Amoevaa dodan kunnuwana suka jiyo min amon muryar ba shiri na dawo daga tunanin dana fada na 'yan daqiqu, Voice din yace dani ina ta magana baka ji na ko? Ina fatan ba dan na fadama sunana da inda nake ba ne ya sanya kayi fushi dani, nayi firgit nace A'a wallahi, amma pls can u repeat it again, hmm muryar tayi daria lokaci guda aka ce I'm Sorry Bana fadar sunana sau uku sai da dalili amma kai har sau biyar na fadama don haka sai dai kai haquri a hirar mu ta gaba Hala na qara fada, kana iya kashe wayar ka tafi massallaci kar na hanaka aiki alkhairi, bye and take care of your self Dear Prince. Nagode, sai anjima ko nace sai Naga kiranki nace amma sai dai hauragiar iska nayi don tuntuni ta kashe wayarta. Mu hadu a 'Yar Mummy (ummin mama) na 2 don jin yadda zata kaya. Prince Ahmad Amoeva 08066038946 #Watsapp Kana iya ziyartar wannan daddalin Dandalin Prince Amoeva Don jin Sauran labarin dama Saura labaruka daban daban

facebook.com

Wata Sabuwa! Gane min hanya, ance Bazazzage ya karanta Fatiha........ Leqa Dandalin Prince Amoeva Don samun labaruka masu nishadantarwa

facebook.com

Aiki Da Hankali... Ba za ka sauka tashar nasara ba sai ka hau motar hakuri da kokari da sadaukarwa. Mutum ya kan kosa da kuruciya, amma idan ya girma zai dawo yana begen ta. Yana karar da lafiyarsa wajen neman kudi sannan ya sa kudi yana neman ta. Rinjayar mai karfi ba shi ne gwaninta ba, Gwani shi ne wanda ya iya bakinsa, ya rinjayi zuciyarsa sannan ya ji tausayin ma su rauni. UWA ITA KADAI CE TA KE MANTA KANTA A ADDUA, TA SHAGALTU DA YI MA DANTA. MU SO IYAYENMU. Wanda ya fi ka wadata ba lalle ne ya fi ka arziki ba. Wadatacce shi ne wanda yake samun biyan bukatunsa. Wahalallu a duniya mutane biyu ne: Wanda Allah ya kawo lokacin abu ya ce ba za ayi shi ba, da wanda Allah bai kawo lokacin abu ba ya ce sai an yi shi. Ka yarda da hukuncin Allah, shi ne zama lafiya a gare ka. Kyau iri uku ne: Akwai kyan jiki, akwai kyan hali, akwai na zuciya. Kyan zuciya shi ke sada ka da Allah. Kyan hali yana sada ka da mutane. Kyan jiki kuwa a kullum sai ya ja maka fitina. Duba tarihin Annabi Yusuf. Zuciyarka ita ce adireshinka. Harshenka shi ne ma'auninka. Gyara zuciyarka sannan ka kula da harshenka. RAYUWA KAMAR KASUWA CE. KA ZAGAYA KA TSINCI DUK ABIN DA KA KE SO AMMA FA AKWAI RANAR DA ZA KA BIYA DUK ABIN DA KA DAUKA. Wanda ya fi kowa girma shi ne wanda bai ganin girman kansa. Wanda ya fi kowa daukaka shi ne wanda yake amfanin mutane. Ba ka sanin dadin lafiya sai idan ciwo ya zo. Ba za ka san dadin zaman lafiya ba sai ka gamu da tashin hankali. Ana sanin dadin haduwa ne idan an rabu. Gode ma ni'imomin Allah wadanda ka sani da wadanda ba ka sani ba. Maganar gaskiya ba lalle ne ta zama mai dadi ba, amma tana da kyau da amfani. Idan kana tafiya babu takalma za ka gamu da wanda ke tafiya ba kafafu. Kalli wanda ka fi shi a kullum sai ka gode ma Allah!. In kayi aboki da makeri to ko wuta bai konakaba to zaka sami hayaki, shiko mai turare komai rowarsa zaka sami kamshi daga kamshinsa. Yi aboki da mutanen kirki. me hankali kema kansa hisabi, to shin me ka aikata yau dinnan? Allah yasa Mudaceee !!! Admin Shazali A Salisu 08066768402

facebook.com

WASA QWA QwAL WA. ::: Daga Bashir El Bash WANNE ABUNE WANNAN?????? :: :: Farine fat! Kamar qanqara. Baqine sitik! Kamar daren marka-marka, Cinsa haramne, Shansa halalne, anfadeshi a Al qur'an, maza na amfani dashi sau 3 a kullum, Mata suna amfani dashi sau 1 tak! Arayuwarsu, harafi 6 da hausa harafi 7 da larabci. :: :: MENENE WANNAN?? Admin 08066038946 Dandalin Prince Amoeva

facebook.com

Quiz